Jaruman Kannywood sun koka da cewa an cire su daga cikin kwamitin rantsar da Tinubu.

Kannywood Actors
Kannywood Actors

Masana’antar fina-finan Arewacin Najeriya, wadda aka fi sani da Kannywood, ta koka kan kin sanya mambobinta a cikin kwamitin rantsar da zababben shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu.

A ranar 29 ga watan Mayu ne aka shirya rantsar da sabon zababben shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a Aso Villa, Abuja.

Masana’antar a madadin mambobinta, ta bayyana rashin jin dadin ta a wata sanarwa mai dauke da sa hannun jarumi kuma mai shirya fina-finai Al-Amin Ciroma.

Sanarwar ta yi nuni da cewa ‘yan Kannywood sun yi kakkausar suka ga yadda ake zabar ‘yan masana’antar fina-finan kudancin Najeriya wato Nollywood a kan ‘yan Arewa musamman fitattun jaruman Kannywood.

A cewarsa, abin mamaki ne yadda fitattun jaruman Kannywood irin su Mansura Isah, Ali Nuhu, Abdul Amart, Jamila Nagudu, da sauran su ba su shiga cikin jerin sunayen ba, duk da cewa sun yi iya bakin kokarinsu a yakin neman zaben jam’iyyar All. Progressive Congress (APC).

 Sanarwar ta kara da cewa “mafi yawan wadanda suka yi fice a masana’antar fina-finan Hausa sun yi yakin neman zaben Tinubu tun kafin babban taron.

“Yawancin fitattun jaruman Kannywood, irin su Mansura Isah, sun yi fice wajen yakin neman zaben ‘Jagaban, tun ma kafin a bayyana shi a matsayin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC.

“Ina tambayar kwamitin riko na Asiwaju me ya sa aka kafa ta ba tare da wani fitaccen dan Kannywood a cikin jerin sunayen ba?

Sanarwar ta kara da cewa "Yawancin 'yan wasan Nollywood da ke cikin jerin ba su ma nuna fuskokinsu ba a lokacin yakin neman zabe da zabe."

Previous News Next News